OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Mako da ya shude

2023: 'Kai dan yawon bude ido ne, a harkar siyasa Cewar Shettima ga Atiku.

2023: 'Kai dan yawon bude ido ne, a harkar siyasa  Cewar She

Mataimakin dan takarar shugaban kasa na jamiyyar All Progressives Congress (APC), Kashim Shettima, ya bayyana dan takarar shugaban kasa na jamiyyar PDP, Atiku Abubakar, a matsayin dan yawon bude ido a harkar siyasa.

 

Ya kara da cewa za su yi masa ritaya zuwa kasar Hadaddiyar Daular Larabawa bayan kammala zaben 2023.

 

Mista Shettima ya bayyana haka ne a wajen gabatar da bikin taron jamiyyar APC ga yan kasuwa da kuma kamfanoni masu zaman kansu a Legas ranar Talata.

 

Ya yi wa tsohon mataimakin shugaban kaca kaca inda ya bayyana matsayar karatun sa.

 

Ya ce takardar shaidar da Atiku ya samu daga Makarantar Kiwon Lafiya ta Kano yace ba wata takarda bace ta azo a gani.

 

Mista Shettima ya kuma soki Atiku kan dadewa da ya yi yana neman shugaban kasa.

 

Ya bayyana cewa Atiku ba Abraham Lincoln, tsohon shugaban kasar Amurka bane, Sai dai a kira shi da Raila Odinga ,wanda yayi kaurin suna wajen shan kaye a zaben shugaban kasa a Kenya.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci