Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB ta kammala shirye-shiryen fitar da sakamakon jarrabawar ta shekarar 2024.
Magatakardar hukumar Farfesa Ishaq Oloyede,ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a Abuja a ranar Litinin mai zuwa.
Shugaban hulda da jama’a na hukumar Fabian Benjamin a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar Lahadin da ta gabata ta nuna alamar za a fitar da sakamakon jarabawar a ranar Litinin.
Za'a fara sakin sakamakon jarabawar daliban da suka fara rubuta jarabawar a kwanakin farko, yayin da wadanda suka rubuta jarabawar a kwanikin karshe za a saki sakamakonsu daga baya.
Tun da farko dai hukumar ta bayyana cewa an yanke shawarar jinkirta fitar da sakamakon na wasu kwanaki ne domin a ba da isasshen lokaci domin tantancewa.
0 Tsokaci