Hoto Daga: Punch
Jami'an tsaro sun yi nasarar ceto wani basarake da aka yi garkuwa da shi a makon da ya gabata a jihar Imo.
A ranar Lahadi ne aka sace basaraken, Acho Ndukwe, na yankin Ihube dake karamar hukumar Okigwe na Jihar Imo.
Haka kuma jami'an su yi ram da mutane 30 da ake zargin masu garkuwa ne da mutane.
Hakan ya faru ne a ranar Litinin yayin wata samame da jami'an suka kai karamar hukumar Orsu da Uli a karamar hukumar Ihiala ta jihar Anambra.
0 Tsokaci