Daya daga cikin yan takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar Ondo, Wale Akinterinwa, ya zargi shugaban kwamitin gudanar da zaben fidda gwannin Usman Ododo da yin magudi a sakamakon zaben.
Akinterinwa ya yi ikirarin cewa anyi magudi Kuma sakamakon zaben fidda gwanin da aka kammala a jihar da aka fitar jabu ne.
Shugaban kwamitin zaben fidda gwani na jam’iyyar APC kuma gwamnan jihar Kogi, Usman Ododo, ya ayyana gwamna Lucky Aiydatiwa a matsayin wanda ya lashe zaben.
Sai dai a wata sanarwa da kakakin yakin neman zaben Akinterinwa, Segun Ajiboye, ya fitar a safiyar ranar Litinin a Akure, ya zargi gwamnan Ododo da zama ya shirya ya kuma rubuta sakamakon zaben.
Mai neman kujerar gwamnan ya kuma bayyana cewa ayyana Aiyedatiwa a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani tamkar almarace da batai kama da hakikanin abunda ya faru ba wajen kada kuri'a.
0 Tsokaci