OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 2 Shekaru da suka shude

APC a Gombe ta zargi Goje da yin zagon kasa kan shiryawa da Inuwa

APC a Gombe ta zargi Goje da yin zagon kasa kan shiryawa da

Photo Source: Ripples Nigeria

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki a jihar Gombe ta zargi Sanata Mohammed Danjuma Goje da yin zagon kasa ga yunkurin shiryawa da gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya.

Jam’iyyar ta kuma ce Goje na neman hujjar ficewa daga jam’iyyar zuwa jam’iyyar PDP saboda kin amincewa da hanyar shiryawa a matsayin dalili.

Jam’iyyar ta nuna rashin jin dadin ta kan matakin da Goje ya dauka na kawo cikas ga shirin zaman lafiya da shugabannin jam’iyyar na kasa ke jagoranta.

Jam’iyyar ta kara da cewa abin takaici ne yadda Goje ya zargi gwamnan da kin amincewa da shirin sulhu.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran jam’iyyar Ambasada Moses Kyari.

Kyari ya yi zargin cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP sun dukufa wajen zawarcin Goje zuwa jam’iyyarsu tare da amincewar sa.

Ya kuma zargi Goje da shirin ficewa daga jam’iyyar APC yayin da ya samu uzurin yin hakan.

Kyari ya ce Goje ya kasance yana nuna kansa a matsayin mai matukar muhimmanci da kuma dacewa a cikin al’amuran jam’iyyar tare da mayar da martabar shugabancin jam’iyyar ba komai ba.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci