An gano sunan ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Enugu ta Gabas a majalisar dattawa, Sanata Chimaroke Nnamani, a matsayin mamba na kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugabancin Najeriya karkashin jam'iyya mai mulki ta APC.
Wannan na zuwa ne yayin da kwanaki kadan ya rage a fara yakin neman zaben shekarar 2023 a hukumance.
Cikin jerin sunayen da APC ta fitar ranar Juma’a, ya kunshi mambobi 422.
Rahotanni na cewa Sanata Chimaroke, wanda aka zaba a karkashin jam’iyyar PDP, an saka shi a matsayin memba Daraktoci da Sakatarorin Daraktoci a cikin jerin sunayen kansilolin.
Idan za'a iya tunawa, dan majalisar ya wallafa wasu sakonni a shafinsa na Twitter, inda ya bayyana Tinubu a matsayin “ ɗan siyasar da ya fi kowa aiki tukuru a wannan zamani”.
Tsohon gwamnan ya yi Allah-wadai da zargin tsohon gwamnan Legas na rashin lafiyarsa, yana mai cewa masu yi wa Asiwaju ba'a ma suna iya samun nasu kason daga baya.
0 Tsokaci