An cire sunan tsohon gwamnan jihar Osun, Rauf Aregbesola daga cikin tawagar yakin neman zabe na jam'iyyar APC mai mulki.
Haka zalika sunayen da aka cire sun hada da tsohon gwamnan jihar Enugu, Chimaroke Nnamani, da na jihar Abia, Orji Uzor Kalu, da kuma Kassim Afegbua, tsohon kwamishinan yada labarai na jihar Edo.
An cire sunayensu ne a cikin sabon sunaye da sakataren jam’iyyar APC na kasa, Iyiola Omisore ya fitar a yammacin Laraba.
Sunayen da aka fitar na farko wanda James Faleke ya fitar a watan Satumba, akwai sunayensu a matsayin mambobin majalisar a sassa daban-daban.
An kafa majalisar ne domin hada kan yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, na zabe mai gabatowa.
0 Tsokaci