Gwamnan jihar Oyo, Engr. Seyi Makinde ya kada kuri'arsa a zaben kananan hukumomi da ke gudana a jihar.
Gwamnan ya kada kuri’a ne a rumfar zabe mai lamba 1, a mazaba ta 11 a karamar hukumar Ibadan ta Arewa maso Gabas da ke Ibadan, babban birnin jihar Oyo.
Makinde ya isa filing zaben da misalin karfe 10:17 na safe kuma ya kada kuri’a bayan mintuna biyar.
Ana gudanar da zaben da hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Oyo, OYSIEC ta shirya a fadin kananan hukumomi 33.
0 Tsokaci