Hukumar shirya jarrabawar shiga jami’a, JAMB, a ranar Litinin din nan, ta fitar da sakamakon jarrabawar ta 2024.
Jarrabawar da aka fara ranar Juma’a, 19 ga Afrilu, ta kare ne a ranar Litinin, 29 ga Afrilu, 2024.
A baya Allnews.ng ta rahoto cewa sama da dalibai miliyan 1.94 ne suka yi rajistar jarrabawar a unguwanni 118 a cibiyoyi sama da 700 a fadin kasar nan.
Magatakardar JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar hukumar dake Bwari a Abuja.
0 Tsokaci