Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi, ya caccaki gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan maganar da ya yi cewar ya taba sa a kamashi a jihar Anambra a shekarun baya.
El-Rufai, a wani taron tattaunawa da kungiyar hadin gwiwa ta Arewa ta shirya a Kaduna ranar Litinin, ya yi ikirarin cewa an taba tsare shi shekaru tara da suka gabata a jihar Anambra na tsawon sa’o’i 48 bisa umarnin Mista Obi.
“A shekarar 2013 na je jihar Anambra a matsayin jami’in jam’iyyar APC domin shaida zaben fidda gwani na gwamna da za a yi a wancan lokacin, Peter Obi a lokacin yana gwamna, ya sa aka kama ni inda aka tsare ni na tsawon sa’o’i 48 a dakina na otal,” cewar Gwamnan Kaduna.
Yanzu a matsayinsa na Gwamna El-Rufai ya ce yana da dukkan karfin iko da zai tunkari dan takarar jam’iyyar LP amma ba zai yi hakan ba saboda kasancewr sa dan Arewa.
A nasa bangaren, Obi ya bayyana kalaman gwamna El-Rufa'i a matsayin wani abinda bai kamata a fito fili ana yada shi ba.
“Abin da mai girma Gwamna Nasir Ahmad El-Rufai ya fada game da ni ya jawo hankalina.Muna girma nauyi na kara hawa kan mu,a wannan gabar ya kamata ace mu dinga hangen nesa,kuma mudinga tauna kalaman mu.
0 Tsokaci