Hukumar kula da yiwa kasa hidima ta NYSC reshen jihar Bauchi, a yau Alhamis ta bayyana cewa mutane hudu na Batch C stream 1 na shekarar 2022, za su maimaita shekarar hidimar su a jihar.
Namadi Abubakar, Kodinetan hukumar a jihar je ya bayyana haka, inda yace za a kara wa wasu mutum 27 shekarar hidima na makonni uku saboda munanan dabi'u da suka nuna lokacin da suke bakin aiki.
Abubakar ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya a Bauchi a lokacin karbar takardar shaidar kammala aikin da ‘yan bautar kasa ke yi.
Ya ce an hukunta wadanda abin ya shafa saboda laifuka daban-daban da suka hada da tserewa da kuma rashin zuwa a lokacin aikinsu.
Mista Abubakar, ya nanata cewa hukumar ba za ta dauki rashin zuwa aiki ba kuma ba za ta yi shakkar hukunta duk wanda ya yi ba daidai ba.
A cewarsa, daga cikin ’yan bautar 1,151 da aka ya ye, biyar daga cikinsu za a karrama su da lambar yabo ta jiha bisa gagarumin gudunmawar da suka bayar wajen inganta rayuwar al’ummar da suka karbi bakuncinsu.
0 Tsokaci