Wasu ‘yan bindiga sun kashe shugaban matasan jam’iyyar APC a karamar hukumar Igbo-Eze ta Kudu a jihar Enugu.
Marigayin mai suna Lucky Idoko ya fito ne daga unguwar Unadu da ke yankin karamar hukumar.
Ya na wakiltan al'umman ne a matsayin Kansila.
Shugaban matasan, wanda shi ne shugaban kungiyar ‘yan banga na yankin, an harbe shi ne a ranar Asabar, a lokacin da yake tafiya a kan babur din haya.
An ce wanda ke tuka babur din ya yi nasarar tsallake rijiya da baya.
Wasu majiyoyi sun ce ana ta cece-kuce a yankin cewa lallai wannan lamari wasu ne suka masa ture.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Enugu, Daniel Ndukwe, ya tabbatar da faruwar lamarin.
“Rundunar ‘yan sandan ta kaddamar da bincike a kan kisan Lucky Idoko,” inji shi.
Lamarin ya faru ne awowi kadan da wasu ‘yan bindiga su ka kai hari a hedikwatar ‘yan sanda da ke karamar hukumar Oji ta jihar.
An kashe mutane biyu ciki har da dan sanda a harin da aka kai a ofishin 'yan sanda.
0 Tsokaci