OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Shekara da ya shude

Na Taba Siyar Da Kadarori Na Don Biyan Tallafin Ilimin Dalibai — Kwankwaso

Na Taba Siyar Da Kadarori Na Don Biyan Tallafin Ilimin Dalib

Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Rabi'u Kwankwaso, ya bayyana cewa wasu kadarorinsa ya ke siyarwa domin cigaba da tallafawa karatu dalibai a jami'a.

 

Inda ya yi alkawarin ci gaba da yin kokari wajen ganin Najeriya ta samu ci gaba.

 

Kwankwaso ya bayyana haka ne a wajen taro karo na 3 wanda kungiyar Kwankwasiyya Development Foundation ta shirya domin bikin cikarsa shekaru 66 a ranar Litinin a Abuja.

 

Tsohon gwamnan jihar Kano ya bayyana ilimi a matsayin jarin ‘yan siyasa da za su sakawa al’umma, inda ya ce ya taba saka hannun jari a fannin ilimi da ci gaban dan Adam saboda tasirin da suke da shi a rayuwar jama’a.

 

Sanata Kwankwaso, wanda ya ce a koda yaushe ya na ba wa kansa abin da zai yi wa mutane, ya ce sama da dalibai 3,000 ne suka ci gajiyar shirin tallafin karatu a shekarar 2011 zuwa 2015 lokacin da ya ke gwamnan jihar.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci