OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Shekara da ya shude

2023: Kwankwaso Ya Kaddamar Da Ofisoshin NNPP a Kebbi

2023: Kwankwaso Ya Kaddamar Da Ofisoshin NNPP a Kebbi

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigerian People’s Party (NNPP), Rabiu Musa Kwankwaso ya kaddamar da ofisoshin yakin neman zabe a jihar Kebbi.

Kwankwaso ya bayyana jin dadin sa kan dimbin magoya baya da suka tarbe shi a jihar. 

Dan takarar shugaban kasan na jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan jihar Kano ya bayyana jin dadin sa a wata zantawa da manema labarai a Birnin Kebbi.

Ya bayyana cewa shi da jam’iyyar sa a shirye suke su tunkari zaben 2023 tare da goyon bayan jama'a a kowace jiha ta kasar nan.

A cewar sa: “Mun yanke shawarar zuwa mu ga abubuwa.

"NNPP ta tsayar da 'yan takarar Majalisun Jihohi, 'Yan Majalisun Tarayya, Majalisar Dattawa da Gwamna a jihar Kebbi kuma goyon baya na da yawa da karfafa gwiwa".

Kwankwaso wanda ya yi magana kan tsare-tsaren sa a fannin ilimi a Najeriya, ya ce yana da tarihin da ‘yan Nijeriya suka shaida a fannin tun lokacin da ya yi gwamna na tsawon shekaru takwas.

Ya kuma bayyana cewa ya ba da fifiko kan ilimi da samar da ababen more rayuwa a tsawon wa’adin sa na shekara takwas a matsayin gwamna.

A cewar sa, ya dauki nauyin daukar ‘yan asalin jihar da waje sama da dubu uku don yin karatu a kasashen waje a fannin likitanci da sauran fannoni.

Ya kara da cewa yana da shirin maimaita hakan a kasar idan ya ci zaben shugaban kasa a 2023.

A lokacin da yake tsokaci kan matsalar rashin tsaro a kasar, ya zargi jam’iyyar adawa ta PDP da jam’iyyar APC, inda ya kwatanta su a matsayin jam'iyya daya.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci