Tsohuwar kwamishiniyar harkokin mata da kananan yara a Zamfara, Haj. Rabi Shinkafi
Kwamishiniyar harkokin mata da kananan yara a Zamfara, Hajiya Rabi Shinkafi, ta ajiye mukamin ta domin karbar makamncin mukamin a jihar Imo.
Hajiya Shinkafi ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasa a yau Alhamis cewa ta ajiye aikin ne domin ta karbi mukamin kwamishiyar a jihar Imo.
Tsohuwar kwamishiniyar ta godewa Gwamna Bello Matawalle da uwargidansa Hajiya A’isha Matawalle bisa bata damar hidimtawa jihar dama kyautata mata.
A cewar ta “Duk rade-radin da ake ta yadawa a kafafen sada zumunta game da murabus na kwata-kwata karya ce; aikin ɓata ne kawai.
“Ina da cikakkiyar dangantaka da gwamna da matarsa. Ina daukar su a matsayin dangina kuma suna cikin hoton tafiyata Imo
Ta tabbatar da cewa Gwamna Hope Uzodinma na jihar Imo da Matawalle sun tattauna a matsayin gwamnonin jam'iyyar APC kuma a matsayin abokai kan batun.
0 Tsokaci