OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 2 Shekaru da suka shude

Gwamnatin Kano Za Ta Gina Wa Fulani Makiyaya Gurin Zama

Gwamnatin Kano Za Ta Gina Wa Fulani Makiyaya Gurin Zama

Kwamishinan tsare-tsare da Kasafi, Nura Muhd ƊanKadai

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa zata tabbatar da wadatar abinci tare da samarwa Fulani makiyaya matsuguni a jihar domin magance matsalar makiyaya/manoma.

 Kwamishinan tsare-tsare da Kasafi, Alhaji Nura Muhd Ɗankadai ne ya sanar da haka lokacin da yake ƙarin haske kan kasafin kudin bana a ɗakin taron ma'aikatar dake sakateriyar Audu Bako.

Ya ce gwamnati ta warewa ɓangaren noma Naira biliyan 5 da miliyan takwas a kasafin na bana domin cimma hakan.

 Kwamishinan jihar, Alhaji Nura Muhammad Dan Kadai ya ce an ware Naira 100,000,000 domin gina ƙauyen Fulani makiyaya a jihr.

Ya ƙara da cewa za'a samar da wurin ajiye dabbobi da hanyoyin kiwo da kuma dam domin  dabbobin a kan Naira  40,000,000.

 Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na daga cikin gwamnonin dake ganin akwai buƙatar Fulani makiyaya su samu matsuguni domin rage hatsarin da sukan tsinci kan su a wasu sassan ƙasar nan dama samarwa ƴan ƴan su ilimi.

Jaridun kasar nan sun rawaito Gwamnan a mabanbanta lokuta yana cewa hakan zai tabbatar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci