Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas, a jiya, ya mara wa Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas baya a karo na biyu, amma ya yi shiru kan makomar ɗan takarar jam’iyyar adawa ta PDP.
Ɗan takaran PDP a jihar Legas wato Dr Olajide Adediran wanda aka fi sani da Jandor, bai samu goyon bayan Gwamna Wike ba.
Gwamna Wike ya yi jawabi ne a matsayin babban baƙo na musamman a taron shekara-shekara na mata a jihar Legas na shekarar 2022, mai taken ‘Spring Forth, Stand Out,’ da aka gudanar a Eko Hotel and Suites, Legas.
Gwamnan ya sanar da bayar da tallafin Naira miliyan 300 ga kwamitin matan masu muƙamai a matsayin tallafi.
Yayin da yake mara bayan ga Sanwo-Olu a karo na biyu, gwamnan Rivers ya ce: “Da yardar Allah za ka zama gwamna a karo na biyu.
"Jihar Legas ta fi sauran jihohin ƙasar nan, saboda Legas ta bai wa mata damar shiga harkokin mulki ta fannoni daban-daban.
"Ina farin cikin shiga wannan taro, ruwaitowar Jaridar Vanguard.
“Ba na wasa da siyasar ƙabilanci, Ko da Sanwo-Olu yana jam’iyyata amma baya yin abu mai kyau, da ban zo ba.
"Ba na nadamar cewa ina goyon bayanka.”
0 Tsokaci