Hukumar kare Muhalli ta Jihar Legas, LASEPA, ta rufe coci-coci, otal-otal, mashaya, da sauran cibiyoyi na wani dan lokaci a sassan jihar, sakamakon yawan hayaniya.
Tokunbo Wahab, Kwamishinan Ma'aikatar Muhalli da Ruwa na Jiha, ne ya wallafa hakan a shafinsa na X a ranar Juma'a.
Yankunan da abin ya shafa sun hada da Ifako-Ijaiye, Abesan Estate, Abule-Egba, Alagbado, Command, da Dopemu.
Daga cikin wuraren da abin ya shafa akwai cocin Katolika, 1602 Hotel, Seventh Heaven Bar & Lounge, Lourita Hotel & Suites, God’s Porch Ministries, Wonderful Bible Prayer Ministries, White Pavilion Hotel, Quest Hotel & Suites, Excel Hotel & Suite, and HoneyComb Confectionery Ltd
Sanarwar ta ce an rufe cibiyoyin na wani dan lokaci don "tilasta bin ka'idojin muhalli.
0 Tsokaci