OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Shekara da ya shude

Zamu Ladabtar Da Ma’aikatan Da Ke Da Hannu Wajen Satar Mai – NSCDC

Zamu  Ladabtar Da Ma’aikatan Da Ke Da Hannu Wajen Satar Ma

Babban kwamandan hukumar tsaron farin kaya ta kasa NSCDC, Dakta Ahmed Audi, ya yi alkawarin Ladabtar da duk wani jami’in da aka samu da hannu a cikin satar man fetur a yankin Neja Delta.

Audi ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da ya ke zantawa da kamfanin dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a birnin tarayya Abuja.

 Ya ce rundunar na gudanar da bincike kan rahotannin da ake zargin wasu ma’aikata da hada hannu da barayin mai a yankin Neja-Delta.

Audi ya ce hukumar NSCDC ta inganta tsarinta da ka’idojin aiki, tare da samar da isassun hanyoyin da za a bi wajen binciken dukkan wanda ake zargi.

Audi ya ce hukumar NSCDC ta inganta tsarinta da ka’idojin aiki, tare da samar da isassun hanyoyin da za a bi wajen gudanar da sahihin binciken.

A cewar Dr Ahmed Audi “Zan so na tabbatar wa ‘yan Najeriya da zarar mun kammala bincike, duk wanda aka samu da laifi za a hukunta shi"

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci