Nigerian Police
Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da cafke wani da ake zargin mai kera bam ne a jihar Taraba.
An kama wanda ake zargin ne a ranar Laraba a Tella, karamar hukumar Gassol ta jihar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Taraba, DSP Usman Abdullahi ne ya bayyana hakan ga manema labarai.
Kayayyakin da aka gano a gidan wanda ake zargin sun hada da sassa daban-daban na kera bama-bamai.
AllNews ta tattaro cewa wanda ake zargin ya yi amfani da gidansa ne a matsayin masana’antar sa na bam.
Bayan kama shi, an kuma kwato makamai da alburusai daban-daban kamar yadda rahotanni suka bayyana.
Duk da cewa ba a bayyana sunan wanda ake zargin ba, jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wanda ake zargin dan jihar Zamfara ne.
A halin da ake ciki kuma an ruwaito cewa yana hannun ‘yan sanda a Jalingo, babban birnin jihar domin ci gaba da bincike.
Ku tuna cewa jihar ta sha fama da hare-haren bama-bamai a cikin watan da ta gabata.
0 Tsokaci