Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta cafke wata mata mai shekaru 30 a hanyar kaiwa ‘yan bindihga makamai da alburusai jihar Zamfara.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ayuba Elkana ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin holin matar a Gusau, inda ya ce an kama matar mai suna Fatima Lawali a ranar Alhamis, 25 ga watan Oktoba da misalin karfe 9:30 na dare.
Kwamishinan ya ce an kama matar da ake zargi da alburusai da bindiga kirar AK-47 daga kauyen Dabagi a jihar Sokoto, zuwa ga wani shugaban ‘yan bindiga, Ado Alero wanada da ya dade yana kai hare-hare yankunan Zamfara da makotan jihar.
0 Tsokaci