Wasu ‘yan bindiga sun yi awon gaba da daliban jami’ar Nsukka (UNN) a hanyar su ta komawa makaranta domin ci gaba da gudanar da harkokinsu na karatu.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 4 na yamma a ranar Lahadi a kan titin Nsukka-Opi, Ekwegbe,karamar hukumar Igbo-Etiti a jihar Enugu, a kudu maso gabashin Najeriya.
PREMIUM TIMES ta tattaro cewa ‘yan bindigar sun yi ta garkuwa da matafiya a kan hanyar tun ranar Asabar.
Ana cigaba da kai re-hare a kan hanyar a ranar Talata, in ji majiyoyin.
Bayan daliban da aka sace har da wasu matafiya.
0 Tsokaci