OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Shekara da ya shude

Kasafin Kudin 2023: Gwamnati Kadai Ba Za Ta Iya Cigaba Da Kula Da Jami'o'i Ba – Buhari

Kasafin Kudin 2023: Gwamnati Kadai Ba Za Ta Iya Cigaba Da Ku

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce gwamnati ita kadai ba za ta iya ci gaba da kula da Jami'o'i a Najeriya ba.

 

Shugaban kasar ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da jawabinsa kan kudirin kasafin kudin shekarar 2023 a gaban taron hadin gwiwa na majalisar dokokin kasar a ranar Juma’a.

 

Buhari ya ce gwamnati za ta samar da wasu matakai na samun kudaden da za a Gudanar da bangaren ilimi yadda ya kamata a Najeriya.

 

Shugaban ya kuma ce za a daina bayar da tallafin man fetur a shekarar 2023.

 

Tun tuni ministan kudi da sauran Masu ruwa da tsaki suke shawartar Gwamnatin Tarayya ta soke tallafin man fetur din da kasar take bayarwa.

 

 A wannan karan Shugaba Buhari ya bukaci naira triliyan 19.76 a kasafin kudin shekarar 2023.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci