Kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta yanke shawarar dakatar da yajin aikin da ta shafe watanni takwas tana yi.
Kungiyar ta dauki wannan matakin ne a taron majalisar zartarwa ta kasa (NEC) da kungiyar ta gudanar a Abuja a safiyar yau Juma’a.
Wani ɗan kungiyar ASUU-NEC da ke wajen taron ya shaida wa Premium times cewa dakatar da yajin aikin ya biyo bayan hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a makon da ya gabata inda ta bukaci kungiyar ta bi umarnin kotu.
Kotun masana’antu ta bayar da umarnin ne bisa gwamnatin Najeriya ta bukaci a umurci malamai da su dakatar da yajin aikin.
Majiyar PREMIUM TIMES ta bayyana cewa har yanzu fa gwamnati ba ta biya bukatun malaman suka nema ba.
0 Tsokaci