OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Mako da ya shude

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Bauchi ta samarwa maniyyatan sama da dubu biyu biza

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Bauchi ta samarwa maniyya

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi, ta ce ta samu bizar maniyyata 2,200 a jihar domin gudanar da aikin hajjin bana.

 

Babban Sakataren Hukumar, Imam Abdurrahman Ibrahim Idris ya bayyana haka a ranar Talata, inda ya kara da cewa jihar na da maniyyata 2,680. 

 

Idris ya bayyana haka ne a lokacin da yake kaddamar da rabon jakunkuna da Unifom ga maniyyatan jihar da aka shirya a hedkwatar hukumar, ya kuma ba da tabbacin hukumar ta himmatu wajen ganin an samar da biza ga sauran maniyyatan a kan kari.

 

 Ya kuma kara da cewa hukumar ta yi dukkan shirye-shirye don fitar da jadawalin tashin jirgin mahajjata. 

 

Jami’in yada labarai na hukumar Muhammad Sani Yunusa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, inda ya bayyana cewa babban sakataren ya bayyana Uniform a matsayin wata shaida ga dukkan mahajjata a lokacin aikin Hajji. 

 

Ya kuma bukaci alhazai da su rika sanya rigar su a kodayaushe tun daga sansanin Hajjin Bauchi har zuwa lokacin gudanar da aikin Hajji a kasar Saudiyya.

 

A cewar Yunusa, shugaban hukumar ya shawarci alhazai da su gaggauta dinka rigar su a kan lokaci, yana mai cewa hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON ta sanya ranar 15 ga Mayu, 2024 don fara jigilar maniyyata zuwa Saudiyya.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci