Nigerian Police force
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kwara, Paul Odama ya tabbatar da sace wani dan sanda mai suna ASP Abdulmumini Yusuf a jihar da wasu ‘yan bindiga suka yi.
Kwamishinan ya ce tuni rundunar ‘yan sandan jihar ta fara gudanar da bincike a yayin da take aikin ceto tare da kamo da kuma gurfanar da wadanda suka aikata laifin.
A cewar sa: "Eh, gaskiya ne, amma har yanzu muna kan aikin."
Jami’in da ke aiki a ofishin shiyya na ‘yan sanda a Ilorin an yi garkuwa da shi ne a daren ranar Talata a lokacin da yake shirin shiga gidan sa.
Wata majiya a yankin ta bayyana wa jaridar Punch a yau cewa kwamishinan ‘yan sandan ya ziyarci yankin.
A cewar majiyar: "Mun lura da cewa an yi ta sintiri da jami'an 'yan sanda a kewayen anguwan sakamakon kasancewar kwamishinan 'yan sandan."
Haka kuma, sakataren kwamitin ba da shawara kan harkokin tsaron na al'umma a jihar, Shola Muse ya koka kan karuwar kalubalen tsaro a cikin jihar yayin da ya yi kira da a kara himma daga hukumomin tsaro domin shawo kan lamarin.
0 Tsokaci