Gwamnan Jihar Katsina
Gwamnatin Katsina ta bayyana janye dokar haramta hawan babura daga bakin karfe goma na dare a duk fadin jihar.
Gwamnan Aminu Bello Masari ne ya bayyana janyewar ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun sa, Aminu Isa ya fitar a daren jiya Alhamis.
Rahotanni sun bayyana cewa an janye dokar ne domin bawa al’umma damar gudanar da ayyukan ibada a watan Ramadana.
Wwatan Ramadana dai lokaci ne da al’ummar musulmi ke yawaita iada, wanda wasu ke tafiya tahajjud a masallatai daban-daban musamman a goman karshe.
Tun da fari dai gwamnatin Jihar Katsina ta sanya dokar hana hawa baburan ne daga bakin karfe goma na dare da a yunkurin dakile kai hare-hare da ‘yan bindiga ke yi.
0 Tsokaci