Shahararren mawaki David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, ya bayyana a ranar Alhamis cewa ba zai sake fitar da waka ba bayan ya kammala wannan album din.
Idan dai za a iya tunawa, Davido ya yi ta yawo a kafafen yada labarai a kwanan baya kan fadan sa ta yanar gizo da mawaki Ayodeji Balogun, wanda aka fi sani da Wizkid.
A wata wallafa da yayi a kafafen sa na sada zumunta yace akwai wasu da suka shirya makarkashiyar ganin bayansa.
Ya wallafa a shafinsa na X "daga album din nan zan daina waka baki daya tunda naga akwai mutane da suka kagu suga sun fitar dani daga masana'antar"
Mawakin a ranar Laraba ya fitar da fefen bediyon wakarsa mai suna "Kante" da suka raira tare da mawakiya Fave.
0 Tsokaci