Governor Darius Ishaku of Taraba State
Gwamnan jihar Taraba, Darius Ishaku ya caccaki ‘yan majalisar dokoki daga jihar da suke yi ikirarin ayyukan gwamnatin tarayya a matsayin nasu.
Gwamnan wanda ya yi magana a yau (Litinin) yayin da yake ganawa da manema labarai a Jalingo ya ce abin bakin ciki ne ganin yadda ‘yan majalisa ke ikirarin ayyukan gwamnatin tarayya nasu ne maimakon su aiwatar da nasu.
A cewar sa, ya zama wajibi masu ruwa da tsaki su gargadi irin wadannan wakilai da ke ikirarin ayyukan da ba su aiwatar da su ba.
A cewar sa, gwamnatin jihar ta lura cewa wasu ayyuka na shiyya da kuma manyan ayyuka da 'yan Taraba suke kallo a matsayin aikin mutum daya maimakon ayyukan gwamnatin tarayya ba haka bane.
Ya kuma koka da cewa: "Tsarin ganin ayyukan gwamnati a matsayin na mutum daya ya zama abin damuwa ga gwamnatin jihar."
Ya kara da cewa "Masu hakan su ne wakilan mu wadanda suka dauke dukiyar mu ta zama tasu."
0 Tsokaci