OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 2 Shekaru da suka shude

Hatsarin Jirgin Ruwa Yayi Sanadin Rasa Rayuka 26 a Jihar Sokoto

Hatsarin Jirgin Ruwa Yayi Sanadin Rasa Rayuka 26 a Jihar Sok

Boat mishap

Akalla mutane 26 da suka hada da mata da yara ne suka rasa rayukan su a wani hatsarin jirgin ruwa a Jihar Sokoto.

A cikin mutanen 26, mata 21 da yara 5 ne suka nitse a kogin Shagari da ke karamar hukumar Shagari ta jihar Sokoto.

Shugaban karamar hukumar Shagari, Alhaji Aliyu Dantani ya bayyana wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata.

Dantani ya bayyana cewa har yanzu ana ci gaba da aikin ceto a kogin.

Ya kuma bayyana cewa ba a iya tantance ainihin adadin wadanda ke cikin jirgin ba.

Ya kara da cewa kwararru a gargajiyance na aikin ceto wadanda suka tsira ko kuma kwato gawarwaki daga kogin.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci