OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Shekara da ya shude

Kwankwaso Ya Gana da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Sufurin Ruwa

Kwankwaso Ya Gana da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Sufurin Ruwa

Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, dan takarar shugabancin kasa a jam'iyyar NNPP, yayi kira ga gwamnati kan gyaran hanyoyin sufuri da suke kaiwa gabar ruwan teku dake Apapa, Jihar Legas. 

Kwankwaso, yayi kiran ne a yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar karkashin jagorancin, Prime Maritime Project.

Dan takarar ya bayyana cewa karsar nan na da bukatar yin shirye-shirye na bunkasa fannonin samar da kudaden shiga musamman, fannin sufurin jiragen ruwa.

A cewar sa: "Na saurari bayanan ku, kuma na fahimci kalubale dake tattare da bangaren sufurin jiragen ruwa a Najeriya.

"Babban misali shine hanyar da ta dangana da gabar ruwa ta Apapa, wanda a wata ziyara dana sami zarafin kawo jihar Legas na gani cinkushe da motocin diban kaya a daidai gadar Ijora dake hanyar.

"A matsayi na wanda ya rike mukamin matekamakin shuagaban majalisar wakilai ta kasa, gwamnan jiha, da kuma na tsohon minista a Najeriya ina da zummar kawo sauyi a fannin abinda ya shafi tsaro, cin hanci da rashawa, da hukumomin tsaro daban-daban dake kasar nan," kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito. 

Shima a jawabin sa, wanda ya jagoranci taron, Kunle Folarin, ya bukaci dan takarar da ya cika alkawurran da yayi ta hanyar kawo gagarumin sauyi a fannin sufurin jiragen ruwa da kasuwanci, wanda aka mai da saniyar ware a ayyuka da gwamnatin Najeriya ke yi.

 

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci