OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Shekara da ya shude

Amurka Da Birtaniya Sun Gargaɗi Yan Kasar Mazauna Najeriya Kan Yiwuwar Hare -haren Ta'addanci

Amurka Da Birtaniya Sun Gargaɗi Yan Kasar Mazauna Najeriya

Kasar Amurka da Birtaniya sun gargadi yan kasarsu mazauna Najeriya kan hare-haren taaddanci a kasar musamman a Abuja babban birnin tarayya.

 

A cewar wani mai ba da shawara kan harkokin tsaro na ofishin jakadancin Amurka a Najeriya, ya ce akwai yiwuwar a kai munanan hare-haren taaddanci a Najeriya, musamman a garin Abuja.

 

Ofishin ya ce wuraren da ake kaiwa hari na sun haɗa da gine-ginen gwamnati, wuraren ibada, makarantu, kasuwanni, manyan kantuna, otal-otal, mashaya, gidajen cin abinci, wuraren wasannin motsa jiki, tashoshin sufuri, wuraren tabbatar da doka da kuma ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa.

 

Sakamakon haka, ofishin jakadancin Amurka ya ce, za ta rage zirga zirgan ta na ayyuka har sai nan gaba.

 

Ta shawarci Amurkawa da ke Najeriya da su guji duk wani tafiye-tafiye ko yawo mara muhimmanci, su kasance idon su a bude, su guje sa cunkoson jama'a, da bin labaran cikin gida da kuma neman shawarwarin hukumomin tsaro.

 

Bugu da kari,Ofishin jakadancin ta shawarci Amurkawa mazauna Najeriya da su sake duba tsare-tsaren tsaron kansu, su rika cajin wayar salulan su saboda lamarin gaggawa in ya taso da kuma daukar shaidar da ta dace.

 

Haka itama Babbar Hukumar Burtaniya ta bayar da irin wannan shawara ga yan kasar ta mazauna Najeriya .

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci