Bauchi state governor, Bala Mohammed| Photo Source: BBC
Kungiyar Limamai da Masu Wa’azin Jihar Bauchi sun nuna goyon bayan su na zarcewar Gwamna Bala Mohammed a matsayin Gwamnan Jihar Bauchi.
Kungiyar ta bayyana cewa duk da suna goyon bayan wa’adin sa na 2 don ci gaban jihar, wata rana za su so ganin ya hau kujerar shugabancin kasan nan.
Haka kuma sun yi nuni da cewa an bar jihar Bauchi a baya wajen cigaba a tsakanin takwarorin ta kafin zuwan Bala.
Shugaban kungiyar Malam Mubarak Mato Baba-Karami ne ya bayyana wa manema labarai hakan a ranar Litinin a Bauchi.
Baba-Karami ya ci gaba da cewa, a yayin da kungiyar ke yi wa Gwamna Bala addu’a, kungiyar ta san cewa mutane da dama sun nuna goyon bayan su ga Bala ya shugabanci kasa a zaben 2023.
Ya kuma yaba wa gwamnan bisa yadda ya inganta fannin lafiya, noma, ilimi da sauran ababen more rayuwa.
0 Tsokaci