Kakakin kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Dino Melaye, ya bayyana cewa da yawa daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar sun daina aikata laifuka domin dan takarar su Atiku Abubakar ya samu nasarar lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2023.
Melaye, wanda ya taba wakiltar mazabar Kogi ta Yamma a majalisar wakilai ta takwas, ya bayyana hakan ne cikin harshen Hausa a yayin wani zama da ya yi da wasu ‘ya’yan jam’iyyar a jihar Kaduna, inda ake ci gaba da yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar.
Ya yin jan wasu ayoyi na Alkur’ani, ya bayyana cewa “Ba zan yi muku karya ba, da yawa daga cikin mu sun daina aikata laifuka saboda Atiku.
Shiyasa Idan muka roki‘Allah’, yake amsa mana.
In Allah ya nufi abu, zai kasance”.
0 Tsokaci