OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 2 Shekaru da suka shude

'Yan Arewa Sun Gudanar Da Zanga-Zanga A Birnin Landan Kan Rashin Tsaro

'Yan Arewa Sun Gudanar Da Zanga-Zanga A Birnin Landan Kan Ra

Wasu 'yan Arewa lokacin da suke gudanar da zanga-zanga a birnin Landan

 

Wasu Arewa dake zaune a birnin Landan sun gudanar da zanga-zanga don nuna bacin ran su kan rashin tsaron dake kara ta’azzara a Najeriya, musamman Arewacin ta.

 

Masu zanga-zangar da suka tun karfe 12:00 rana na Alhamis sun ce yadda ake kashe ‘yan Arewa ba tare da shugabanni sun yi wani katabus wajen hana hakan baa bin takaici ne matuka.

 

Masu Zanga-zangar sun bayyana takaicin su kan yadda ake kashe yan Arewa ba tare da shugabanni sun dau wani kyakkyawan yunƙuri na dakatar da kisan ba.

 

Cikin wadanda suka jagoranci Zanga-zangar akwai fitaccen lauyan nan Barista Audu Bulama Bukarti da fitaccen dan jarida Ja’afar Ja’afar.

Dan Jarida Jafar Jafar

Masu zanga-zangar sun zargi shugaban kasa, Muhammadu Buhari a matsayin wanda baya daukar shawarwarin kan yadda za’a samar da tsaron.

 

Sun bukaci shugaban kasar da wadanda nauyin magance matsalar ya rataya a wuyan su da su gaggauta daukar matakan sace da kuma kashe ‘yan Arewar da a kullum.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci