Photo Source: PremiumTimes
Bayan wani harin da ‘yan bindiga suka kai wani kauyen Kaduna, an kashe mutane 15.
‘Yan bindigan sun kai hari kauyen Hayin Kanwa da ke Yakawada a karamar hukumar Giwa a ranar Lahadi.
Hakan na faruwa ne kwanaki uku bayan wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane 50 a karamar hukumar.
Wani da ya nemi a sakaya sunan sa yace an yi jana’izar mutanen ne a ranar Litinin.
Ya Kuma koka da yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara ganin yadda ake samun mace-mace a kullum tun ranar Alhamis.
Wani dan banga kuma ya shaida wa Daily Trust cewa, “Al’amarin ya yi muni saboda wasu ‘yan bindiga sun kashe karin mutane 15 a Hayin Kanwa a daren jiya Lahadi.
Rahotanni sun ce ‘yan bindigan sun kai hari kan al’ummar garin suna harbe-harbe, inda ya ce gawarwakin mutanen da suka mutu a harin da aka kai a daren Lahadin sai da safe aka kwashe su.
Wata majiyar kuma ta yi zargin cewa ‘yan bindigan a yanzu sun fi sha’awar kashe mutane akan sace su.
Gwamnati ko ‘yan sanda ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.
0 Tsokaci