OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Shekara da ya shude

Hukumar EFCC ta kama wasu ma’aikatan banki 12 bisa zargin zamba

Hukumar EFCC ta kama wasu ma’aikatan banki 12 bisa zargin

Jamian Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Taannati (EFCC) sun kama wasu maaikatan banki 12 bisa zargin zamba a jihar Enugu.

 

A cikin wata sanarwa da ta fito a ranar Asabar, ta hannun mai magana da yawun Hukumar Wilson Uwujarem, ya ce jamianta shiyyar Enugu sun kama wadanda ake zargin ne a ranar Jumaa.

 

Ta ce binciken farko ya nuna cewa wadanda ake zargin sun sace wasu kudade a wasu asusu da aka dade ba a yi amfani da su ba a reshen wani tsohon banki a jihar.

 

Hukumar ta bayyana sunayen wadanda ake zargin, Anthony Odeniyi, Onyekachi Deki, Oguchukwu Ene, Chizaram Elendu, Uchenna Anyakora, Kingsley Onah da Elizabeth Akwe.

 

Sauran sun hada da, Victoria Ezedie, Obinna Chidi-Ukah, Uzochukwu Etoh, Harrison Udeze da Chinenye Acibe.

 

Hukumar ta EFCC ta kara da cewa "Za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu da zarar an kammala bincike."

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci