OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 2 Shekaru da suka shude

Gwamnatin Kaduna Ta Sake Yi Wa Malamai 35,000 Jarabawar Kwarewa

Gwamnatin Kaduna Ta Sake Yi Wa Malamai 35,000 Jarabawar Kwar

Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufa'i| Hoto Daga: BBC

Gwamnatin jihar Kaduna ta sake yin gwajin kwarewa ga malaman firamare 35,000 a yunkurin ta na inganta ilimi a jihar.

Hakan na zuwa ne kusan shekaru hudu da gwamnatin tayi irin wannan jarabawar wanda ta kori malamai 22,000 sannan ta dauki kwararru 25,000.

A cewar shugaban hukumar kula da ilimi na SUBEB, Tijjani Abdullahi, jarabawar ba wai don a kori malami ba ne, sai dai a gano gibin da ake da shi a fannin darussa da nufin horar da malamai. 

Tijjani ya bayyana hakan ne yayin kaddamar da jarabawar da aka gudanar ta na'ura mai kwakwalwa a cibiyoyi uku a jihar.

Ya kara da cewa malaman "za su ga banbanci a tsarin jarabawar na bana." 

Zaku tuna cewa Gwamnatin ta sallami malamai sama da 20,000 a shekarar 2017 sakamokon faduwar jarabawar cancantan da suka yi.

Hakan ya jawo cecekuce a tsakanin jama'a wanda har kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC) ta nuna adawa ga gwamnatin jihar.

Daga bisani Gwamnatin ta dauki kwararrun malamai 25,000 don rufe gibin da aka samu.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci