OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Mako da ya shude

Gwamnatin Adamawa ta rufe makarantu sanadiyar barkewar cutar Kyanda

Gwamnatin Adamawa ta rufe makarantu sanadiyar barkewar cutar

Gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya bayar da umarnin rufe makarantun sakandare a fadin jihar saboda barkewar cutar kyanda.

 

 Shugaban riko na hukumar kula da makarantun gaba da firamare na jihar Adamawa Samuel J. Wagereng ne ya bayar da wannan umarni a ranar Litinin. 

 

Sanarwar ta ba da umarnin a ci gaba da rufe dukkan makarantun har zuwa ranar Litinin 13 ga Mayu, 2024.

 

 allnews.ng ta tattaro cewa makarantun sun bukaci daliban su da su dawo a yau 6 ga watan Mayu 2024 domin cigaba da karatu kamar yadda aka saba saidai sanarwar ta dage komawar zuwa sati mai zuwa.

 

 Wani bangaren sanarwar yace "Ya kamata makarantu su kasance a rufe har zuwa mako mai zuwa ranar Litinin 13/5/2024 saboda barkewar cutar kyanda a fadin jihar, wannan umarni ya hada har da makarantu masu zaman kansu"

 

 Idan za'a iya tunawa Allnews.ng ta rawaito a ranar Juma’a ne aka tabbatar da mutuwar mutane 42 daga kamuwa da cutar kyanda a kananan hukumomi biyu na jihar.

 

 Kwamishinan lafiya da ayyukan jin kai na jihar, Felix Tangwami wanda ya tabbatar da hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Yola, babban birnin jihar ya bayyana cewa ma’aikatar ta samu rahoton mutum 131 sun kamu da cutar a Mubi da kuma 177 a kananan hukumomin Gombi.

 

 Ya ce: “Barkewar ta shafi mazaba 8 a Mubi da mazabu 7 a Gombi inda adadin wadanda suka mutu ya kai 42 dag acikin 131.

 

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci