Ebonyi State governor, David Umahi| Photo Source: PremiumTimes
Gwamnan jihar Ebonyi, David Nweze Umahi ya amince da karin girma ga ma’aikatan gwamnati na shekarar 2019, 2020 da kuma 2021.
Amincewar za ta yi tasiri ne kawai ga ma’aikatan gwamnati da suka cancanta a jihar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da wayar da kan jama’a na jihar Ebony, Hon. Barr Orji Uchenna Orji ya fitar a ranar Litinin.
Gwamnan ya kuma amince da biyan duk ‘yan fansho a jihar.
Sanarwar ta kara da cewa biyan kudin zai fara aiki ne daga ranar Talata, 22 ga Maris na 2022.
0 Tsokaci