Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran siyasar Kwankwasiyya, Rabi'u Musa Kwankwaso ya zama dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar New Nigeria People's Party (NNPP).
An bayyana Kwankwaso ne a matsayin zababben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2023 a ranar Laraba a Abuja.
Wakilan jam’iyyar sun yanke wannan shawara ne ta hanyar sanarwa kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Babban taron jam’iyyar na kasa dai an gudanar ne a filin wasa na Moshood Abiola dake Abuja.
Idan dai za a iya tunawa, shugaban jam’iyyar na kasa, Dakta Boniface Aniebonam ya bayyana cewa taron zai bayyana kwankwaso a matsayin dan takarar jam’iyyar a zaben shugaban kasa na 2023.
Aniebonam wanda ya bayyana a wani taron manema labarai a ranar Juma’a, 3 ga watan Yuni ya ce Kwankwason “za a tsayar da shi ba tare da hamayya ba. Kwankwaso bawan Allah ne."
0 Tsokaci