Prince Adewole Adebayo
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP), Prince Adewole Adebayo, ya ce matsalolin Najeriya sun wuce gona da iri, inda ya sha alwashin kawo karshen talauci cikin watanni 18 da kuma bunkasa tattalin arzikin kasar.
Adebayo ya kuma ce kasar za ta ci gaba da tunkarar kalubalen da take fuskanta a halin yanzu, sai dai idan har ta samu shugabanci na gaskiya da rikon amana.
A cewar sa, matsalolin yan tada kayar baya da ‘yan fashi da makami na ci gaba da ta’azzara ne saboda rashin sahihancin manufa daga shugabannin kasar, yana mai cewa, “Abin da muke kira matsalar tsaro a Najeriya ita ce matsalar yau da kullum, a Najeriya muna fama da fadace-fadace kawai. daga 'yan fashi.
‘’Duk wata matsala da bindigar AK47 za ta iya magancewa ba matsala ba ce, gwamnati ba ta so ta kawo karshen matsalar ne kawai,babu wani abu mai tsanani a wajen gwamnatin, Sojojin Najeriya suna da karfi sosai.
"A kiyasin da nayi, ina ganin sojojin Najeriya na amfani da kashi biyu cikin dari na hankalin su kan Boko Haram domin sun ga ba shi da muhimmanci ga gwamnati.
“Suna da mutane da yawa da suke samun kudi da wadannan abubuwa,wasu ma har cewa sukeyi bari na shigesu domin nan ba da jimawa ba zan yi ritaya ba za su biyani fansho ba kuma wannan Wawayen a nan suna neman Naira biliyan 1 a mako, don haka bari in shigesu. . Abin da ke faruwa ke nan. ‘Yan fashi suna samun kudi, jami’an tsaro suna samun kudi. Abin da ke faruwa ke nan.
shugaban gidan Talabijin na KAFTAN ya kara da cewa, ''Ina da shirin samar da ayyuka miliyan 30. Lokacin da mutane suka samu aikin yi kuma ka sanya mutane a makaranta, za ka samar da masu tsaka-tsaki da kuma magance matsalar talauci. Aikin ya zo da masauki da sauran abubuwan karfafawa to, talauci zai kau."
0 Tsokaci