OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 2 Shekaru da suka shude

An Gudanar Da Addu'ar Samun Nasarar Zama Shugaban Kasa Ga Bola Tinubu A Kano

An Gudanar Da Addu'ar Samun Nasarar Zama Shugaban Kasa Ga Bo

Bola Ahmed Tinubu

Tsohon dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Bebeji/Kiru ta Kano, Abdulmuminu Jibrin Kofa ya ce Bola Ahmed Tinibu zai tsaya takarar shugabancin Najeriya a kakar zabe ta 2023.

Abdulmuminu Jibrin Kofa ne ya sanar da hakan a ranar Asabar din da ta gabata yayin da yake ganawa da manema labarai jim kadan bayan kammala addu’ar shiga sabuwar shekara ta 2022 ga kasar nan.

A cewar Kofa, “A halin yanzu, babu wanda ya cancanci ya jagoranci Najeriya kamar Tinubu, idan aka yi la’akari da matsayin da yake da shi a kasar nan.

Ya kara da cewa ba sai an tallata Tinubu a APC ba.

Sama da malamai 2,500 karkashin jagorancin babban limamin Kafin-Maiyaki ne suka halarci taron addu’o’in da aka gudanar a kauyen Kofa da ke karamar hukumar Bebeji a jihar Kano da misalin karfe 11:30 na safe.

 

Jim kadan bayan an gama addu’o’in,  Kofa ya bayar da tallafin karatu ga  mata 2,500 tare da bawa wasu matasa 2,500 tallafin bayan sun samu horo kan sana’o’i daban-daban a karkashin shirin sa.

Da yake jawabi, Kofa ya ce an gudanar da addu’o’i na musamman din ne domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar da kuma samun nasarar Bola Tinubu a zabe mai zuwa.

Da yake magana kan sulhu tsakanin tsohon gwamnan Kano Rabi’u Musa Kwankwaso da Dr Abdullahi Umar Ganduje, Abdulmuminu Kofa ya ce, “Ba abin mamaki ba ne a ce an sulhunta Kwankwaso da Ganduje ganin cewa sun dade suna tare don haka idan aka sasanta.

Ya ce sasancin zai ciyar da Kano gaba.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci