Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun yi garkuwa da tsohon kwamishinan gidaje da tsara birane, Injiniya Babangida Abubakar Idris a jihar Adamawa.
An harbe wasu mutum biyu har lahira yayin harin da aka kai gidan tsohon kwamishinan a ranar Talata.
Masu garkuwa da mutanen sun kewaye gidan da ke unguwar Bajabure a karamar hukumar Girei ta jihar.
AllNews ta tattaro cewa an harbi tsohon kwamishinan ne a kafa kafin a tafi da shi yayin da wasu da dama suka samu raunuka.
A halin da ake ciki wata majiya na kusa da iyalen sa ta bayyana cewa masu garkuwa da mutanen sun bukaci a biya su kudin fansa naira miliyan 30 a ranar Laraba.
Wata majiya da ba a bayyana sunanta ba ta ce tsohon kwamishinan ya tsallake rijiya da baya a wani hari da aka kai masa a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyar APC a jihar.
Majiyar ta ce, “Abin tashin hankali shi ne, a lokacin zaben fidda gwani na APC da ta gabata, ya tsallake rijiya da baya, inda wasu mutane suka kai masa farmaki inda suka farfasa gilashin motarsa."
Kakakin rundunar ‘yan sanda a Yola, SP Suleiman Nguroje ya ce rundunar ta samu rahoton yayin da take tabbatar da faruwar lamarin.
Nguroje ya ce tuni rundunar ta fara aikin ceto.
0 Tsokaci