Wata kungiya a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta yi kira da a tsige gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi a matsayin kodinetan majalisar matasa a yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar.
Kungiyar ta masu goyon bayan Shugaban kasa (PSC), ta ce ya kamata a cire Mista Bello daga mukamin da aka basa sannan a sauya kujerar zuwa kudu.
A makon da ta gabata ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, ya bayyana sunan gwamnan jihar Kogi a matsayin kodinetan wayar da kan matasa na majalisar yakin neman zaben sa.
Kassim Muhammad, shugaban kungiyar, a wata sanarwa da ya bayyanawa manema labarai a ranar Litinin, ya ce kasancewar Mista Bello yana adawa da kudurin karba-karba hakan yasa wannan matsayi bai dace dashi ba.
Kassim ya kara da cewa yahaya Bello ba ya cikin jerin matasa, a nemi wani mukami daban a bashi amma ba kodinetan matasa ba.
0 Tsokaci