Wata babbar kotun tarayya da ke Sokoto a ranar Larabar da ta gabata ta bayar da umarnin a tsare wani darakta a hukumar kula da kayayyaki ta jihar Sokoto, Hassan Bello, a gidan gyaran hali bisa zargin badakalar naira miliyan 1.3 na aiki.
Mai shari’a Ahmad Mahmud shi ne, ya bayar da umarnin a tsare Hassan Bello bisa kamasa da laifi.
Mista Mahmud ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 4 ga watan Oktoba, domin cigaba da sauraren karar neman belin da kuma shari'a.
Hannafi Sa'ad ma'aikaci a Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ya shaida wa kotu cewa wanda ake tuhuma ya aikata laifin ne tun a watan Agustan shekarar 2021.
Ana zargin Bello, wanda shi ne Daraktan gudanarwa na hukumar da karbar kudaden ne daga hannun Aliyu Adamu-Tsaki, Yusuf Abubakar da Yahaya Salihu a gaban Dahiru Muhammad a Sokoto.
EFCC ta yi zargin cewa wanda ake tuhumar ya gabatar musu da takardun aiki na karya wanda daga baya aka gano na karya ne kuma babu su.
NAN
0 Tsokaci