OTHER SERVICES

Connect with us

  • Hausa News
  • Updated: 1 Shekara da ya shude

Magoya Bayan Peter Obi Sun Yi Watsi Da Umarnin ‘Yan sanda, Sun Gudanar Da Gangami A Legas

Magoya Bayan Peter Obi Sun Yi Watsi Da Umarnin ‘Yan sanda,

Magoya bayan Peter Obi sun bijirewa umarnin ‘yan sanda yayin da suka yi gangamin magoya baya a kofar Lekki Toll Gate dake birnin Legas a ranar Asabar.

Duk da 'yan sandan da aka baza a kan titi, magoya bayan Peter Obi sun haifar da cunkoson ababen hawa da safe yayin da motoci masu zaman kansu da direbobin bas suka nemi wasu hanyoyin da za su bi.

 Wani direban da ya zanta da jaridar Punch ya bayyana yanda lamarin ya auku “Mutanen Peter Obi Sun kashe hanya, na dad'e a Cikin cunkoso kafin in samu hanyar wucewa Amman daga baya jami'an tsaro sun zo wajen domin tabbatar da masu gangamin sunbi Umarnin kotu"

Idan za'a iya tunawa a kwanakin baya kotu Yankee hukuncin Dakatar da magoya bayan jam'iyyar labour party daga gabatar da gangamin da suka shirya gabatarwa tun da fari.

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta tura ‘yan sandan Rapid Response Squad (RRS) zuwa kofar shiga Lekki domin dakatar da gangamin da magoya bayan Peter Obi sukayi.

 Kakakin ‘yan sandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin, ya ce an baza jami'an yan Sanda a wajen taron domin tabbatar da komai ya tafi bisa tsarin doka.

Batu

Join our Telegram platform to get news update Join Now

0 Tsokaci