Dr Mustapha Sule Lamido
Gabanin zaben gwamna na 2023, jam'iyyar PDP ta jihar Jigawa ta kaddamar da tawagar yakin neman zaben mai adadin mutane 27.
Tawagar kamfen din ta samu halartar dan takarar gwamna na jam’iyyar, Dr Mustapha Sule Lamido a Dutse ranar Litinin.
Lamido ya jaddada bukatar tawagar su ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukan su.
Tawagar za ta gudanar da aikin yakin neman zaben dan takarar gwamna na jam’iyyar a fadin kananan hukumomi 27 na jihar.
Tawagar za ta kasance karkashin jagorancin Isah Ahmad Duniya Ba Hutu.
A nasa jawabin, Ba Hutu ya yi kira ga ‘yan kungiyar da su hada kai wajen ganin jam’iyyar ta samu nasarar lashe zaben 2023.
Ya kuma yi alkawarin yin aiki bisa ka’idojin jam’iyyar domin samun nasarar jam’iyyar.
0 Tsokaci