Mahukunta sun ce gobarar ba tayi muni ba
Wata Gobara ta tashi a hedikwatar ma'aikatar kudin kasar nan dake babban birnin tarayya Abuja ta kone abubuwa da dama.
Kawo wannan lokaci ba’a san musabbabin gobarar ba, sai dai tuni ma’aikatan kwana-kwana suka kai agajin shawo kan ta.
Kakakin hukumar kashe gobara ta FCT, Abraham Paul ya ce ma'aikatansu na can suna ƙoƙarin kashe wutar, kamar yadda jaridar punch ta wallafa.
A wani saƙo da ma'aikatar kuɗi da kasafin ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce gobarar ba ta yi muni ba kamar yadda aka yi ta zuzutawa a shafukan sada zumunta inda ta ce wasu batira ne da aka keɓe suka kama da wuta a wani zaure da ke ƙasa a cikin hedikwatar ma'aikatar.
0 Tsokaci