Hoto Daga: PremiumTimes
Sakamokon kisa da aka yi wa wasu makiyaya biyu a garin Ashige da ke karamar hukumar Lafiya a jihar Nasarawa, jama'a na zaman dar-dar.
Rahotanni sun nuna cewa wasu 'yan bindigan da ba'a san ko su waye ba ne suka kashe makiyayan.
An tsinci gawarwakin ne a cikin wata gona tare da raunin yanka daban-daban a fuskokin su.
Lamarin da ya faru a daren jumma'a dai ya jefa mutane cikin firgici.
Tuni aka kai gawarwakin asibitin kwararru na Dalhatu A`râf dake garin na Lafia.
0 Tsokaci